September 22, 2023

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Gwamnatin tarayya ta yi barazanar cewa za ta sallami dukkan jami’an lafiyar da suka kauracewa bakin aikinsu da sunan yajin aiki.

1 min read

Ministan lafiya na kasa Dr Osagie Ehanire ne ya bayyana hakan a jiya Litinin yayin tattaunawarsa da tawagar da gwamnatin tarayya ta kafa tare da shugabannin kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta kasa a birnin tarayya Abuja.

Yayin tattaunawar tasu, ministan ya yi barazanar ne yana mai cewa, duk wani likitan kasar nan da aka samu bai halarci wurin aikinsa ba a yau Laraba, to za a sallame shi.

Dr Osagie Ehanire, ya kuma umarci shugabannin asibitoci da su bude rijistar daukar bayanan ma’aikatan da ke zuwa aiki tun daga karfe 7:00 na safe zuwa 12 na ranar kowacce rana.

Haka kuma ya kara da cewa, za a dauki kwakkwaran mataki kan duk ma’aikacin da aka samu da aikata laifin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *