Saudiyya za ta sassauta dokar kulle daga ranar Lahadi
2 min read
v
Saudiya ta ce zata cire dokar kulle a fadin kasar tare bude harkokin kasuwanci nan da ranar Lahadi, a wani matakin sassauta dokar duk da cewa ana kara samun masu kamuwa da cutar.
Za a janye dokar kullen daga karfe 6:00 safe na kasar tare da barin ci gaba da sallah a masallatai da bude kasuwanni a kasar.
Jiragen kasa da kasa za su ci gaba da kasancewa a dakace, an kuma hana taron sama da mutum 50 a waje daya, in ji gwamnatin kasar.
Har yanzu hukumomin kasar ba su bayyana ko za a yi aikin hajji wannan shekarar ba, wanda kusan mahajjata miliyan biyu ne ke zuwa ko wacce shekara a fadin duniya.
Har yanzu ana samun masu kamuwa da cutar korona a Saudiyya, wadda ke da sabbin masu cutar da suka kai 3,941 cikin sa’a 24, wanda ya kai adadin masu cutar a kasar 154,233.
Har zuwa ranar Asabar, kasar na samun masu cutar korona sama da 4,000 kwana shida a jere.
Akwai wadanda suka mutu 1,230 ya zuwa yanzu a kasar, tare da karin sanar da mutum 46 a ranar Asabar.
Zuwa yanzu gwamnati ba ta ce komai ba game da batun.
Moyo ne na biyu da ya fuskanci tuhumar cin hanci daga cikin ‘yan majalisar ministocin Shugaba Emmerson Mnangagwa.
Ya hallara a kotun cikin wata motar ƙasaita da gwamnati ta ba shi tare da rakiyar hadimansa, kamar yadda wakilin BBC a Harare, Shingai Nyoka ya bayyana.
Yayin shari’ar, an tuhume shi da laifuka daban-daban na karya ƙa’idojin ofishinsa sannan aka umarce shi da ya bayar da fasfonsa na tafiye-tafiye.
Ana sa ran zai sake bayyana a gaban kotun nan da ƙarshen watan Yuli.