September 22, 2023

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

A Nigeria Karin samun mutume 661 sun kamu da korona.

1 min read

Ƙididdigar ta kuma nuna cewa cutar korona ta ƙara kashe mutum 19 cikin sa’a 24 a ƙasar, inda yanzu yawan waɗanda suka mutu sanadin cutar tun bayan ɓullarta a Najeriya, suka kai 506.

Cikin alƙaluman da hukumar ta fitar daren Asabar ta ce cutar korona ta sake kama mutum 230 a Legas, jihar da annobar ta fi tsanani a Najeriya.

Amma daga cikin waɗanda aka tabbatar da sun kamu da cutar 19,808 a Najeriya, an sallami waɗanda suka warke 6718 daga cibiyoyin killace majinyatan cutar, bayan an tabbatar da warkewarsu.

Alƙalumman sun ce ƙarin mutum 127 suka kamu da cutar a jihar Rivers, a Delta kuma mutum 83, yayin da kuma aka sake gano mutum 60 da korona ta shafa ranar Asabar a Abuja, babban birnin ƙasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *