March 28, 2024

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Ana zaman dar-dar bayan ‘yan bindiga sun kashe mutune 21 a Jihar Zamfara.

1 min read

Bayanan baya-bayan nan daga jihar na nuna cewa akalla mutum 21 ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon harin ‘yan fashin daji a ranar Asabar.

Mutanen garin sun ce mahara fiye da 200 ne a kan babura suka auka wa garin tare da buɗe wuta kan mai uwa-da-wabi lokacin da suka yi yunkurin artabu da su.

Wani mutumin Ruwan Tofa ya shaida wa BBC cewa daga cikin mutanen da aka kashe har da wata mace ɗaya, da kuma namiji 20, yayin da aka jikkata ƙarin mutum goma sha biyar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara dai ta ce zuwa yanzu ta tabbatar da mutuwar mutum goma ne sakamakon wannan hari na yammacin Asabar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *