September 22, 2023

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Coronavirus a Najeriya: Mutum 544 sun sake kamuwa a Najeriya

1 min read

Alkalumman da hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta fitar ranar Lahadi sun nuna cewa cutar ta kara kashe mutum 11 cikin sa’a 24.

Yawan mutanen da a hukumance annobar korona ta shafa yanzu sun kai 28,711 a Najeriya, yayin da kuma adadin wadanda cutar ta kashe suka kai 645 tun ɓullarta a ƙasar.

Adadi mafi yawa na masu korona da aka sake samu, ya fito ne daga Lagos, jihar da cutar ta fi ƙamari a Najeriya, inda mutum 199 suka sake kamuwa. kuma Yanzu yawan masu korona a jihar ya kai 11,244.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *