Ana fargabar yaɗuwar cututtuka daga dabbobi zuwa mutane
1 min read
Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa cutukan da ke yaɗuwa daga dabbobi zuwa mutane na ci gaba da karuwa, kuma za a cigaba da fuskantar hakan matsawar ba a ɗauki matakin kare dabbobi da kuma gandun daji ba.
An ɗora laifin cututtukan masu yaɗuwa kamar cutar korona kan yadda ake yawan dogaro da samun sinadari mai gina jiki daga dabbobi da ayyukan noma da kuma sauyin yanayi.
Rahoton hukumar bincike kan muhalli ta Majalisar Ɗinkin Duniya ya gano cewa a duk shekara irin wadannan cutuka da dabbobi ke shafawa mutane na kashe mutun miliyan biyu a duk shekara.
Sannan annobar korona za ta janyo mummunan hasara ga tattalin arzikin duniya dala tiliyan tara tsawon shekaru biyu.
Cutar Ebola da Sars har ma da cutar Korona dukkaninsu daga dabbobi suka yaɗu zuwa ga mutane.