September 22, 2023

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Shugaban Nigeria Buhari ya ce zai binciki kudaden Naija.

1 min read

hugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ya sha alwashin gano matsalar da ke durkusar da ci gaban yankin Neja-Delta a kudu maso kudancin kasar, duk da irin dumbin dukiyar kasa da ake sadaukarwa yankin duk shekara.

Shugaban ya bayyana hakan ne a shafinsa na tuwita a ranar Alhamis da yamma, inda ya kara da cewa ”wannan gwamnatin a shirye take wajen kawo ci gaba cikin gaggawa kuma mai dorewa a yankin.”

Wannan batu na shugaban na zuwa ne a ranar da wasu jami’an tsaro suka zagaye gidan Joy Nunieh – tsohuwar shugabar Hukumar Raya Yankin Neja Delta NDDC, tare da ƙoƙarin kutsawa gidan nata don kama ta, kan wasu zarge-zarge.

Duk da cewa Shugaba Buhari bai ambaci batun Nunieh ba, amma a sakon nasa ya ce ya fayyace wa Majalisar Dokoki da hukumomin bincike da na tsaro cewa su yi kokarin yin aiki tare da juna, domin a samu damar tabbatarwa da kuma cimma gaskiya da yin ƙe-ƙe da ƙe-ƙe a harkar arzikin ƙasa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *