NNPC zai gyara matatun man kasar nan
1 min read
Kamfanin main a kasa NNPC ya bayyana cewa dukannin matattun main a kasar nan zasu fara aiki a tsakiyar shekarar 2023.
Shugaban kamfanin Mele Kyari ne ya bayyana hakan a wani shirin talabijin da aka gudanar tare da shi a birnin tarayya Abuja, yana mai cewa kamfanin na iya bakin kokarin sa don ganin wannan yunkuri ya tabbata.
Mele Kyari ya kuma kara da cewa bangarori masu zaman kansu ne zasu yi hadin gwiwa da kamfanin waje gudanar da aikin gyaran matatun, da suka jima basa aiki.
Najeriya dai na da matatun mai Guda uku da ke Warri da Fatakwal da kuma Kaduna sai dai sun sahfe tsahon shekaru basa aiki.