May 13, 2024

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Wani Matashi ya hallaka Wani Mutum a Karamar hukumar Kumbotso a nan Kano

1 min read

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta tabbatar da cafke wani matashi mai suna Haruna Ya’u mai shekaru 20, bisa zargin hallaka wani mai suna Sani Ibrahim mai shekaru 22 ta hanyar caka masa almakashi a kirji.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Kano DSP. Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce al’amarin ya faru ne a unguwar Dantsinke dake karamar hukumar Kumbotso a nan Kano.
Haka zalika rundunar ta sanar cewa, matashin yanzu haka, yana sashen rundunar domin ci gaba da fadada bincike.

2 thoughts on “Wani Matashi ya hallaka Wani Mutum a Karamar hukumar Kumbotso a nan Kano

  1. Shima a yanke masa hukuncin dan haka addini ya umarta,hakan shizai hana alumna yawan barna ,amma rashin zartar da hukunci shiyakesawa ake cigaba da taaddanci.daga Abu Ayshat

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *