Hadimin Shugaban Kasa Garba Shehu ya ce”gwamnati na daukar matakai kan tsadar kayan masarufi
1 min read
Hadimin Shugaban kasar,ya bayyana haka ne,a Wata hira da yayi da Wata kafar yada labarai a jiya a kano.
Garba shehu ya ce manoma da ‘yan kasuwa a kasar,Su ne ke da hannu wajen haddasa tashin tsadar kayan masarufin.
Farashin Shinkafa a Nigeria na kara tashi a kasuwanni
A ‘yan kwanakinnan, dai farashin shinkafa yayi tashin gwauran zabi a Nigeria,inda a kasuwanni da dama ana siyar da shinfada ta gida dubu 25.
To sai wasu na ganin tashin farashin dalla ne,ya haddasa tsadar kayan masarufin Nigeria.
A gefe guda masana tattalin arzikin kasa na cewa, rufe iyakokin kasar ne kawai,zai kawo sassauci ga matsalar.