Gwamnatin tarayya ta umarci gwamnatin Kano ta sake bude cibiyoyin gwajin Korona
1 min readGwamnatin tarayya ta umarci jihar Kano da sauran jihohin kasar nan da su sake bude dukkanin dakunan gwaje-gwajen Covid-19 da aka rufe a baya.
Bustandaily ta ruwaito shugaban kwamitin kartakwana na fadar shugaba kasa kan annobar Covid-19 Boss Mustapha ne ya bada umarnin biyo bayan bullar annobar a karo na biyu ranar Talata
Boss Mustapha ya.
Ya ce rahotanni da ke iskesu ya nuna cewa mafiya yawa daga cikin cibiyoyin gwaje-gwajen basa yin aiki yadda ya kamata.
Ya kuma ce daga ranar daya ga watan janairun shekara mai kamawa za a fara bayyana sunayen matafiyan da suka ki yadda a yi musu gwajin na Covid-19.
Masarautar Rano ta dakadar da dagatai biyu da suka sace tallafin Korona
Idan za a iya tunawa dai tun a ranar 14 ga Disambar da muke ce ne cutar covid-19 ta sake bullowa a karo na biyu.
Hakan kuma ta sanya tuni hukumomi suka fara daukan mataki domin ganin bata yadu kamar yadda ya yi a farkon zuwanta ba