March 29, 2024

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Sojoji sun kubutar da mutum 10 da aka sace a Kaduna

1 min read

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da kubutar da mutane 10 da aka sace kusan makwanni biyu da suka gabata a gidajen ma’aikatan Hukumar Kula da Filin Jirgin Sama ta Tarayya (FAAN) da ke karamar Hukumar Ikara.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida a jihar, Samuel Aruwan, ya ce a ranar Laraba ne sojojin na Najeriya suka ceto mutane 10.

Mista Aruwan, wanda ya yi wa yan jarida bayani game da ci gaban da aka samu a fannin tsaro na jihar, ya ce ba za a iya bayar da cikakken bayani game da wurin da aka kubatar da mutanen ba saboda dalilan tsaro.

An kubutar da wasu daga daliban Kaduna da aka sace
‘Yan bindiga sun sace ɗalibai 30 daga kwalejin gandun daji da ke Kaduna
A ranar juma’ar da ta gabata ne yan bindiga suka kai hari bayan da suka fasa katangar rukunin gidajen inda suka awon gaba da mutun 1
Bayan wannan hari ne yan bindigar suka shiga cikin kwalejin gandun daji da ke kusa da Mando inda suka yi awon gaba da mutum sama da talatin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *