Sheikh Ibrahim Khalil: Dalilina na ficewa daga jam’iyyar APC
1 min read
Sheikh Ibrahim Khalil, fittacen malamin addinin Musulunci kuma shugaban majalisar malamai a Kano ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC.
Malam Ibrahim Khalil ya sanar da ficewar tasa ce daga APC a daidai lokacin da jam’iyyar ke fama da rikici tsakanin bangaren Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da Sanata Ibrahim Shekarau.
Shehin malamin ya shaida wa BBC cewa: “To ni a matsayina na dan jam’iyyar APC kuma daya daga cikin dattawa da kuma daya daga cikin caucus, abin da nake so in tabbatar shi ne na fita daga jam’iyyar APC.”