APC za ta fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa a watan Mayu
1 min readJam’iyyar APC ma mulkin Najeriya ta ce za ta gudanar da zaɓukan fitar da ‘yan takara a muƙamai daban-daban a watan Mayun 2022.
Jam’iyyar za ta fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa ranar 30 ga watan Mayu.
Za a fara zaɓuakan ne da na ‘yan majalisar jiha a ranar 17 ga Mayu, yayin da da na ‘yan majalisar wakilai zai biyo baya ranar 19, sai kuma na ‘yan majalisar dattawa ya gudana a ranar 21.
Zaɓen fitar da ‘yan takara a muƙamin gwamna zai gudana ne ranar 24 ga watan na Mayu.