Rundunar Yan sandan Kano ta musanta labarin da Gwamnatin Kano ta fitar na cewa karfe ne ya fadowa Dan jarida ba Harbin bindiga ba
1 min readWannan bayani da rundunar yan sandan ta fitar ya musanta ikirarin gwamnatin Kano cewar wani karfe ne daga gini da ake yi a fadar gwamnatin ya raunata ɗan jaridar.
Mai magana da yawun gwamnan Kano Sunusi Bature Dawakin Tofa a sanarwar da ya fitar ya musanta cewa harsashine, to sai dai rundunar yan sanda ta tabbatar da batun harsashin
Kwamishinan ƴan sandan Kano CP Muhammad Hussaini Gumel a tattaunawarshi da kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya tabbatar da cewa harsashine ya raunata ɗan jaridar, amma sun bincika bindigogin jami’an ƴan sandan dake aiki a fadar gwamnati kuma babu wani harsashi da ya fita daga cikinsu.
Hakan na nuna cewar harsashin daga wani wurin ya dira a fadar gwmanatin Kano.