Gwamnatin tarayya ta ce za ta tallafawa kananan hukumomin kasar nan domin ragewa al’umma radadin talaucin da suke fama da shi a yanzu.
Ministan ayyuka na musamman Sanata George Akume ne ya bayyana hakan lokacin da ya karbi bakuncin shugaban hukumar tsara yadda ake kashe kudaden gwamnati Victor Morakwu a ofishinsa a Abuja.
George Akume ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da su samar da hanyoyin saukakawa rayuwar al’ummar dake zaune a karkara.
Ministan ya kara da cewa wannan shirin na daya daga cikin alkawuran da shugaba Buhari ya dauka na fitar da mutane miliyan dari daga kangin talauci.