Dole ne dalibai su koma Makaranta gobe Litinin -Kano
1 min readKwamishinan ilimin na Jihar kano Sunusi Saidu ya karyata labarin da ake yadawa cewa an fasa komawa Makaranta gobe Litinin.
Kwamishinan ya ce Makarantun kwana zasu koma a yau Lahadi 17 ga wata yayin da makarantun jeka ka dawo su kuma a Ranar Litinin 18 ga wata.
Yayi Kira ga iyaye su kaucewa amfani da kafafan sada zumunci dake yada labarin karya.