May 16, 2024

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Gwamnatin Jihar Kano ta ce Babu fashi komawar Dalibai Makaranta a gobe

1 min read

Gwamantin jihar Kano ta ce babu fashi makarantun jihar za su koma a gobe litinin 18 ga watan Janairun 2021.

Kwamishinan ilimi na jihar Muhammad Sunusi Sa’idu Kiru ne tabbatar da hakan a Lahadin nan.

Ya ce, daga Lahadin gwamnati ta ba da umarnin bude makarantun kwana yayin da daliban jeka-ka-dawo za su koma a gobe Litinin.

A don haka ya bukaci iyaye da su yi watsi da jita-jitar da ake yadawa kan rashin komawa makarantun a gobe.

Kiru ya Kuma ce, tuni ma’aikatar ilimi ta fitar da jadawalin karatu na shekarar 2021.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *