May 13, 2024

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Gwamnatin Jihar ta ce hutun Sabuwar Shekara bai shafi dalibai masu rubuta WAEC ba

1 min read

Gwamnatin jihar Kano ta ayyana yau Alhamis a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan jihar domin murnar zagayowar sabuwarshekarar musulunci.

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan yada labarai na Kano, Malam Muhamamd Garba ya fitar.

Haka zalika ma’aikatar ilimi ta Kano ta ce wannan hutu bai shafi daliban masu zana jarrabawar WAEC ba kamarba cewar kwamishinan ilimi na Kano Sanusi Sa’idu Kiru
a wata zantawa da yayi da ‘yan jarida.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *