‘Yan Sandan Kano sun kama masu kwacen 41 a jiya
1 min readRundunar ƴan sanda ta jihar Kano ta kama wasu matasa 41 waɗanda ake zargi da ƙwacen waya.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ƴan sandan jihar Kano DSP. Abdullahi Haruna Kiyawa shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a jiya.
DSP
Kiyawa ya ce, ana zargin matasan ne da tare hanya a daren Asabar a daidai mahaɗar titin Ɗanagundi da ke ƙaramar hukumar Birni da Kewaye inda suka riƙa karɓe wayoyi a hannun mutane.
An samu matasan da babura guda huɗu da wuƙaƙe manya da ƙananan da kuma miyagun ƙwayoyi a cewarsa.
Wasu mutane ne dai suka bawa rundunar bayanai na sirri Wanda hakan ya baiwa rundunar nasarar kama matasan