Marayu da zaurawa sama 150 sun amfana da tallafin Abinci -Usman Dalhatu
1 min readKungiyar tallafawa marayu da zaurawa dake Unguwar Medile ta raba kayan abinci ga mutane sama da dari da hamsin a jiya a Asabar.
Shugaban Kungiyar Kwamared Usman Dalhatu ne ya bayyana Haka a yayin zantawar sa da manema labarai.
Alhaji Usman Dalhatu ya Kara da cewa suna samun tallafin ne daga hannun jama’a da Kuma manyan kungiyoyi dake sassa da dama.
Ya Kuma bayyana Kira ga sauran mawadata dasu himmatu wajen cigaba tallafawa marayu da sauran masu bukata ta musamman.
Wasu daga cikin mutanan da suka amfana da tallafin sun bayyana farin cikin su bisa tallafin.