May 21, 2024

Bustan Daily

Trusted Source for Online News Publishing

Ko Sabon Mai Horos da Super Eagles zai iya daukar Yan wasan gida

1 min read

Hukumar kwallon kafar Najeriya, NFF ta nada Finidi George a matakin sabon kociyan Super Eagles.

George, ya yi wata 20 yana aikin mataimakin Jose Santos Peseiro, wanda ya ajiye aikin, bayan kammala gasar cin kofin nahiyar Afirka da Super Eagles ta yi ta biyu a Ivory Coast a bana.

Haka kuma ya ja ragamar tawagar Najeriya a matakin kociyan rikon kwarya a wasan sada zumunta biyu da ta buga a Morocco a watan jiya.

Ya doke Ghana 2-1 a wasan farko, hakan ya kawo karshen rashin nasara a kan Black Stars daga Super Eagles cikin shekara 18, amma an doke shi 2-0 a karawa da Mali a wasan na sada zumunta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *